Jam’iyyar APC ta amince Ganduje ya ci gaba da jagorancinta

FB IMG 1740590462486

Abdullahi Umar GandujeAsalin hoton,OTHERS
Jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya ta kaɗa ƙuri’ar amincewa da salon jagorancin shugabanta, Abdullahi Umar Ganduje.

A taron da jam’iyyar ta kammala yau Laraba a Abuja, masu ruwa da tsaki na jam’iyyar sun yaba da rawar da Ganduje ya taka tun bayan naɗa shi kan muƙamin a watan Agustan 2023.

Hakan na nufin cewa tsohon gwamnan na jihar Kano zai ci gaba da jagorancin jam’iyyar har zuwa lokacin da za a yi babban taronta na ƙasa, inda za a zaɓi cikakken shugaba.

A watan Agustan 2023 ne kwamitin gudanarwa na jam’iyyar ya tabbatar da Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar na riƙo na ƙasa, bayan ajiye aikin shugaban jam’iyyar da ya gabace shi, Sanata Abdullahi Adamu.

BBC

Domin samun sauran shirye-shiryen  Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo nan  👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/IqPyC2oGzdQ9NudcMXFqHZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *