Karshen Alewa! Kasar Chadi Ta Yanke Huldar Tsaro Da Faransa,

Faransa Da Chad

Kasar Chadi ta ba da sanarwar kawo karshen yarjejeniyar ayyukan sojan da ta sabunta da Faransa a shekarar 2019.

Gwamnatin Chadin ta ce ta dauki wannan matakin ne da nufin jaddada ‘yancin kanta shekaru 66 bayan samun ‘yancin kai daga turawan mulkin mallaka.

Hakan na faruwa a wani lokacin da Rasha ke kara kusantar kasashen Afirka kamar yadda a ranar Alhamis ma’aikatar tsaron Nijar ta ce ta karbi tallafin makamai daga hukumomin Moscow.

Mininistan harakokin wajen Chadi Abderaman Koulamallah ya bayyana a wannan sanarwa a ranar Alhamis yana cewar, gwamnatin Chadi ta dauki matakin dake kawo karshen yarjejeniyar ayyukan tsaro a tsakanin kasar da Faransa.

Sannan ta ce matakin ya biyo bayan dogon nazari a game da wannan yarjejeniya da kasashen biyu suka sabinta a ranar 5 ga watan Satumban 2019.

Ganin yadda matakin ke zuwa a washegarin ziyarar ministan harakokin wajen Faransa Jean Noel Barrot a N’djamena, manazarta na fassara abin a matsayin bazata.

Gwamnatin Chadi ta ce shekaru 66 bayan samun ‘yancin kai daga turawan mulkin mallaka lokaci ya yi da za ta jaddada wannan ‘yanci a zahiri ta kuma sake tantance abokan huldarta a muhimman fannoni wadanda kuma ke daidai da bukatun kasar.

Hakan ba ya nufin an zo karshen huldart a da Faransa kwata-kwata, wannan sabon matsayin na shugaba Mahamat Deby abu ne da ke janyo ayar tambaya.

Wannan al’amari da za a iya kiransa sabon babi a huldar Chadi da uwar gijiyarta wato Faransa abu ne da ke bayyana a wanil okacin da abokiyar hamayyar Faransar wato Russia ke kara samun shiga a yankin Sahel, wanda ko a jiya Alhamis kafar talbijan mallakar gwamnatin Nijar ta gwada wasu kayayyakin da ma’aikatar tsaron kasar ta karba a matsayin tallafin da Moscow ta aike don karfafa matakan yaki da ta’addanci.

Faransa da ke fuskantar koma baya a fannin diflomasiya a ‘yan shekarun nan msamman a tsakaninta da kasashen da ta yiwa mulkin mallaka na shan suka sakamakon girke sojoji a irin wadannan kasashe ciki har da Senegal.

Shugaban kasar Bassirou Diomaye Faye a hirarsa da wasu jaridun Faransar a jiya Alhamis ya kafe kan bakansa a batun kare ‘yancin kan Senegal abin da yake ganin ba zai cika ba muddin Faransa na ci gaba da girke dakarunta.

VOA Hausa

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news zaku iya bibbiyarmu ta 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *