Kotu Ta Bayar da belin Abubakar Malami (SAN) da iyalansa akan kudi Miliyan 500 tare da wasu Sharruda.

IMG 121019 07126 1767784236979

Kotun Tarayya da ke Abuja ƙarƙashin Alƙali Emeka Nwite ta amince da bayar da belin tsohon Babban Lauyan Ƙasa kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, tare da matarsa da ɗansa kan kuɗi ₦500m kowannensu.

Kotun ta shimfiɗa ƙa’idoji masu tsauri, inda ta umarci kowanne daga cikinsu ya kawo mutane biyu da za su tsaya musu, masu filaye a Maitama, Asokoro ko Gwarimpa, tare da miƙa takardun filayen domin tantancewa, da kuma ajiye fasfofinsu a kotu.

Malami na fuskantar tuhume-tuhume 16 na halasta kuɗaɗen haram da EFCC ta shigar, lamarin da ya shafi ma’amaloli da ake zargin darajarsu ta kai kusan naira biliyan 9, yayin da kotu ta ɗage sauraron shari’ar zuwa 17 ga Fabrairu, tare da umartar a ci gaba da tsare shi a gidan gyaran hali na Kuje har sai an cika sharuɗɗan beli.

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *