Kotun Shari’ar Musulunci Ta Aike Da Ramlat Yar TikTok Gidan Gyaran Hali

FB IMG 1708040596510

Daga Aminu Bala Madobi

Kotun Shari’ar Musulunci da ke Kano ta Aike da Ramlat jarumar TikTok  zuwa gidan yari kan zargin badala da karuwanci.

Alfijir labarai ta rawaito a daren Juma’a ne Mai Shari’a Sani Tanimu Hausawa na kotun Musuluncin da ke unguwar Sharada ya sa a ajiye Ramlat a gidan gyaran Hali bayan Hukumar Hisbah ta gurfanar da ita.

A kwanakin nan ne wani bidiyon Ramlat ta ya karade soshiyal midiya, wanda a ciki take tallata madigo, har ta bayyana kanta a matsayin mai wannan dabi’ar.

A cikin bidiyon, an ji matashiyar na cewa, duk wanda zai aureta dole sai ya amince cewa ita za ta auro tata matar, lamarin da ya jawo ce-ce kuce

A kunshin karar laifukan da ake zargin ta da su laifuka ne da suka saba da sashe na 341 da 275 da 227 na Kundin Pinal Kod.

Wacce ake zargin ta amsa laifukan inda ta nemi afuwar kotu bisa laifukan da ta aikata,sai dai saboda kurewar lokaci kotun ta dage shari’ar zuwa ranar 19 ga Fabrairu don yanke hukunci.

Haka kuma kotun ta yi umarnin tisa keyar Ramla zuwa gidan gyaran hali har zuwa ranar da za a sake dawowa gabanta

 
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H3iC9eVfJI012LJzvCQn5V

Slide Up
x

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *