Ku dinga tallafawa wadanda suke a gidan gyaran hali da tarbiyya – In Ji Haj Azumi Namadi Bebeji.

IMG 20241226 WA0960

An bukaci al’umma musammam mawadata da kuma ‘yan kungiyoyin cigaban al’umma da su dinga taimaka wadanda aka daure a gidajen a gidan ajiya da gyaran hali a fadin jihar Kano.

Bukatar hakan ta fito ne ta bakin shugabar kwamitin yiwa daurarru afuwa a jihar Kano hajiya Azumi Namadi Bebeji a zantawar ta da manema labarai. Sakamakon ban kwana da shekarar 2024.

Ta ce gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf na sane da daurarrun kasancewar akwai tanade-tanade da ya ke yi masu.

Ta kuma yabawa gwamnan da mataimakin sa, kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo bisa yadda su ke gabatar da ayyukan alheri ga al’ummar jihar.

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news zaku iya bibbiyarmu ta 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *