Masarauta: Gwamnan jihar Adamawa ya nada sabbin Sarakuna

FB IMG 1735903508158

Gwamna Ahmad Fintiri na Jihar Adamawa ya amince da naɗin sabbin sarakuna da hakimai bakwai a masarautun Jihar.

Nadin sabbin sarakunan ya fara aiki ne nan take, kamar yadda gwamnatin jihar ta sanar.

Sabbin sarakunan sun hada da; Alhaji Sani Ahmadu Ribadu a matsayin Sarkin Fufore, da Ahmadu Saibaru a matsayin Sarkin Maiha, da Barista Barrister Alheri B. Nyako a matsayin Tol Huba da Farfesa Bulus Luka Gadiga a matsayin Mbege Ka Michika.

Sauran su ne Dakta Ali Danburam a matsayin Ptil Madagali, da Aggrey Ali a matsayin Kumun Gombi, da John Dio a matsayin Gubo Yungur.

Gwamnan ya bayyana cewa an zaɓo su ne bisa cancanta ya kuma buƙace su da kasance masu gaskiya da riƙon amana.

Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *