Wani barawo da ba a kai ga gano shi ba ya sace sadaki a aljihun wakilin Ango a yayin daurin aure a masallacin Juma’a na Usman Bin Affan dake Gadon Kaya.
Alfijir labarai ta ruwaito babban limamin Masallacin, Sheikh Aliyu Yunus ya gano hakan yayin da aka bukaci wakilin Angon ya gabatar da Sadakin inda aka nemi kudin aka rasa.
Wata majiya mai tushe ta shaidawa jaridar Nigerian Tracker cewa wakilin Angon ya bada hakuri inda ya nemi limamin ya daura auren tare da alkawarin kawo sadakin daga baya.
A addinin Musulunci dai an amince da daura aure yayin da aka bada Sadaki nan take ko a ka dau alkawarin bayarwa daga baya.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj