Daga Aisha Salisu Ishaq
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da sauye-sauyen shugabanci a jami’o’in gwamnatin tarayya da dama da su ka hada da Jami’ar Abuja l, wacce a yanzu ake kira da Jami’ar Yakubu Gowon. Waɗannan canje-canjen sun fara aiki na nan take.
A Jami’ar Yakubu Gowon, wacce a da sunan ta Jami’ar Abuja, Tinubu ya rusa majalisar gudanarwar jami’ar baki daya tare da sauke Farfesa Aisha Sani Maikudi daga mukaminta na shugabar jami’ar inda aka maye gurbin ta da Farfesa Lar Patricia Manko a matsayin riko na tsawon watanni shida.
Sanata Lanre Tejuoso, wanda a halin yanzu shine babban shugaba a Jami’ar Aikin Gona ta Makurdi, an kai shi Jami’ar Yakubu Gowon s matsayin Babban Shugaba jami’ar.
Sanata Joy Emordi, wacce a yanzu ita ce shugabar jami’ar ilimi ta Alvan Ikoku za ta gaje shi a Makurdi.
Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news zaku iya bibiyarmu ta nan 👇
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇
https://chat.whatsapp.com/IqPyC2oGzdQ9NudcMXFqHZ