Yan Ta’addan Boko Haram sun kai hari kan sansanin sojoji a jihar Yobe

FB IMG 1746352330043

Rahotonni daga arewa maso gabashin Najeriya na cewa mayaƙan Boko Haram sun kai hari kan wani sansanin soji a jihar Yobe.

Jaridun Najeriya sun ruwaito cewa ƴan bindigar sun ƙaddamar da hari kan sansanin soji na ”27 Task Force Brigade” da ke garin Buni Yadi, a yankin ƙaramar hukumar Gujba da tsakar daren Asabar.

Harin na zuwa ne kwana guda bayan ƙungiyar gwamnonin arewa maso gabashin ƙasar sun gudanar da taro a Tamaturu, babban birnin jihar da nufin magance matsalolin yankin, ciki har da matsalar tsaro.

A baya-bayan nan mayaƙan Boko Haram da na ISWAP na neman dawo da hare-hare a yankin.

A cikin makon nan ma ƙungiyar ISWAP ta ɗauki alhakin wani hari da yayi sanadin mutuwar mutum 26 a jihar Borno.

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news ku shiga nan  👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zNrcNKD

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *