Ƙasar Saudiyya ta bai wa Najeriya kyautar tan 100 na dabino

IMG 20250218 113721

Daga A’isha Salisu Ishaq

Saudiyya ta bai wa gwamnatin Najeriya kyautar tan 100 na dabino a matsayin tallafin da ta saba bayarwa duk shekara.

Wata sanarwa da ofishin jakadancin ƙasar a Najeriya ya fitar ranar Litinin ta ce tallafin kyauta ce daga Sarki Salman na Saudiyya.

Sanarwar ta ƙara da cewa jakadan Saudiyya a Najeriya, Faisal Al-Ghamdi, shi ne ya jagoranci miƙa kyautar, wadda aka bayar ta hannun ƙungiyar King Salman Humanitarian Aid and Relief Centre (KSrelief) domin taimaka wa talakawa.

“Jakada Al-Ghamdi ya yi bayanin cewa a wannan shekarar an ba wa Abuja tan 50, Kano ma tan 50,” in ji sanarwar.

BBC

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news zaku iya bibiyarmu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/IqPyC2oGzdQ9NudcMXFqHZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *