Ambaliyar Ruwa Ta Sake kashe Mutane 10 Ta Kuma Lalata Gidaje Da Gonaki

Alfijr ta ra rawaito Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Bauchi, SEMA, ta tabbatar da mutuwar mutane 10 sakamakon ambaliyar ruwa da ta lalata gidaje da gonaki da dama a fadin jihar.

Alfijr Labarai

Daraktan tsare-tsare, bincike da kididdiga a hukumar Adams Nayola, ya tabbatar da hakan a wata hira da Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN a yau Laraba a Bauchi.

Ya ce lamarin ya tilastawa mazauna yankin samun mafaka a wasu wurare Cavan daban

Adams kara da cewar, hukumar na ci gaba da tattara bayanai kan filayen noma da gidajen da su ka lalace a faɗin jihar.

“Akalla mutane 10 ne suka rasa rayukansu yayin da ya tafi da hektoci da dama na gonaki da gidaje a wasu sassan jihar.

Alfijr Labarai

“Kananan hukumomin da abin ya fi shafa sun hada da Jama’are, Giade, Misau, Dambam, Zaki, Darazo, Kirfi, Itas-Gadau, Shira, Gamawa da Toro.

“Duk da cewa ambaliyar ta shafi kananan hukumomi 19 cikin 20 na jihar Bauchi, matsalar ta fi ƙamari a kananan hukumomi goma sha biyu ne kawai,” in ji Nayola.

Slide Up
x

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *