Bayan jirgin Max Air ya tunkuyi ƙasa a filin jirgin saman Malam Aminu Kano ayyuka sun dawo daidai yanzu

FB IMG 1738156072389

Daga A’isha Salisu Ishaq

Ayyukan sauka da tashin jiragen sama sun dawo daidai, bayan tsaikon da aka samu na wasu sa’o’i sakamakon faduwar da jirgin saman kamfanin Max Air ya yi a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano da ke jihar Kano.

A daren Talata ne jirgin ya tunkuyi ƙasa yayin sauka a filin, inda tayoyin sa su ka kone garin saukar.

Sai dai ba a samu asarar rayuka ko jikkata a haɗarin ba.

Da ya ke bayani ga wakilin Daily Nigerian Hausa, wani babban jami’i a filin jirgin saman na Kano, wanda yx nemi a sakaya sunan sa, ya ce al’amura sun daidaita kuma tuni ma aka janye jirgin daga kan titin jirgi.

Ya ce tun misalin ƙarfe 4 na asuba aka janye jirgin.

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news zaku iya bibiyarmu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/IqPyC2oGzdQ9NudcMXFqHZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *