Budaddiyar Wasika Daga Obasanjo Zuwa Shugabannin Najeriya

Obasanjo

Tsohon Shugaban Kasa, Olusegun Obasanjo, ya jaddada cewa yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya zai samu nasara ne idan aka fara daukar mataki daga manyan jami’an gwamnati.

Obasanjo ya nuna cewa yaki da cin hanci a matakin shugabanci zai zama misali ga sauran mutane kuma zai nuna jajircewar gwamnati wajen tabbatar da gaskiya da inganci.

Alfijir Labarai ta rawaito Obasanjo ya bayyana hakan ne a yayin wata tattaunawa ta Zoom a daren Lahadi da aka yi wa lakabi da “Boiling Point Arena.”

Tattaunawar, wadda aka yada ta wasu gidajen rediyon masu zaman kansu a Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun, ta mayar da hankali kan tarihin Obasanjo a gwamnati da yadda yake kallon Najeriya a yanzu.

Obasanjo ya bayyana cin hanci da rashawa a matsayin wata cuta mai matsala mai yawa wadda ta tsoma al’ummar Najeriya cokin wani katonrami, yana mai jaddada cewa dole ne yaki da cin hanci ya fara daga shugabanci domin samun nasara.

“Hanyar da ta fi dacewa wajen yaki da cin hanci ita ce fara daga shugabanci, a nan ne yakar cin hanci zai fara,” in ji Obasanjo.

Tsohon Shugaban Kasar ya kuma bayyana cewa yaki da cin hanci dole ne ya zama na yau da kullum, domin dakile shi daga tushe.

Ya kira da a canza tsarin daukar ma’aikata da nada shugabanni a ofisoshin gwamnati, yana mai jaddada cewa ya kamata a yi nadin shugabanni bisa cancanta, ba bisa tsarin siyasa ko kabilanci ba.

A kan shugabanci, ya ce shugabannin da suka tashi daga kansu ko kuma wadanda aka kafa ta hannun mugun hali, ba za su yi nasara ba.

Ya kara da cewa, Allah ne kawai ke nada shugabanni, kuma wanda ya nadi zai samu nasara.

Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *