Dan Takarar Gwamna Abba Kabir Ya Maka Gwamna Abdullahi Ganduje A Kotu

Alfijr ta rawaito Dan takarar gwamnan Kano a jam’iyar NNPP Abba Kabir Yusuf ya yi karar gwamnatin Kano Abdullahi Umar Ganduje a gaban wata kotu bisa siyar da filin wasa na mahaha da kuma katangar filin wasa na Sani Abacha dake unguwar kofar mata.

Alfijr Labarai

Abba Kabir ya shigar da karar ne karkashin wasu lauyoyi, inda ya zargi gwaman da cefanar da wasu kotunan musulunci biyu a nan Kano.

Sauran wadanda  ake karar sun hada da kwamishinan shari’a na jihar Kano da hukumar kasa da safayo.

Da ya ke zantawa da Premier Radio a madadin Abba Kabir Lauyansa Barista Bashir Yusuf Tudun Wuzurci ya zargi gwamnan da cefanar da wuraren ne saboda son rai da biyan bukatar kansa

Alfijr Labarai

Ya ce gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje na wuce gona da iri wajen siyar da irin wadannan wurare masu amfani ga al’ummar jihar Kano.

Baya ga wannan kuma masu karar sun yi korafi kan siyar da wasu kotunan shari’ar musulunci zuwa ga wasu dai-daikun mutane, wanda shima suke ganin hakan ya sabawa dokar kasa.

Masu karar dai sun shigar da ita ga babban  babban mai shari’a na Kano, Justice Nura Sagir, wanda kuma ya sanya ranar 10 da 11 ga  Nuwamba domin fara sauraran karar.

Premier Radio

Slide Up
x

3 Replies to “Dan Takarar Gwamna Abba Kabir Ya Maka Gwamna Abdullahi Ganduje A Kotu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *