Gwamnatin tarayya ta bayyana Litinin 16 ga watan Satumbar a matsayin ranar hutun Maulidi, don karrama bikin zagayowar ranar haihuwar Annabin tsira Muhammad (S.A.W).
Alfijir Labarai ta rawaito ministan harkokin cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana hakan, a madadin Gwamnatin tarayya, in da yayi amfani da damar wajen taya al’ummar musulmi na gida Najeriya dana kasashen ketare murnar wannan biki mai alfarma.
Ministan ya kuma bukaci al’ummar musulmi da su yi amfani da lokacin wajen yada halayen nagartu tsakanin abokan zama don samun wanzuwar zaman lafiya a kasa ba ki daya.
Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj