Alfijr
![](https://alfijr.com.ng/wp-content/uploads/2022/03/images28729-1-650x365.jpeg)
Hukumar kiyaye hadari ta kasa FRSC reshen jihar Kano, ta ce titin Kano zuwa Zaria ya kasance wurin da hukumar ke fuskantar kalubalen masu ababen hawa, yadda suke tukin ganganci a kan hanyar da a halin yanzu ake gyarawa.
![](https://alfijr.com.ng/wp-content/uploads/2022/03/IMG_20220212_150753-5-1-650x141.jpg)
Zubairu Mato wanda shine babban kwamandan hukumar FRSC ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano.
Ya kuma koka da yadda masu ababen hawa da ke bin hanyar suna gudun wuce gona da iri, wanda hakan kan haifar da munanan hadari a hanyar.
Alfijr
Mato ya ce, ya tura jami’ansa kan hanyar da kayan aikinsu domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a.
![](https://alfijr.com.ng/wp-content/uploads/2022/03/images28629-650x359.jpeg)
Kwamandan ya cigaba da cewa rundunar ta samu nasarar tantance hadurran da ba a taba samu ba a kan hanyar Kano zuwa Bauchi da Kano zuwa Azare da dai sauransu.