Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta (INEC) Ta Ce, Ta Kashe Magudin Zabe A Najeriya.

Alfijr ta rawaito Mutiu Agboke, sabon kwamishinan zabe na jihar Osun, ya ce an yi magudin zabe a Najeriya a baya, amma a halin yanzu babu dama.

Agboke yayi magana ne a ranar Asabar a Osogbo, babban birnin Osun, yayin da yake jawabi ga ma’aikatan hukumar zabe mai zaman kanta.

Ya ce yin magudin zabe ba zai yiwu ba a tsarin da ake yi a yanzu, musamman yadda aka bullo da tsarin tantance masu kada kuri’a.

Hukumar ta INEC REC ta ce fasahar BVAS ta kashe duk nau’in magudin zabe a kasar a halin da ake ciki.

“Aikina shi ne na tabbatar da kimar INEC, kuma darajar INEC ita ce ta tabbatar da an kirga kuri’un jama’a a zaben da za a gudanar,” inji shi.

Ya ƙara da cewa, “Ina so in tabbatar wa masu zabe a jihar cewa ba za mu hana su samun sakamakon kuri’u ba, kuma amfanin kuri’unsu shi ne su kada kuri’a ta hanyar da ta dace, kuma su samu sakamako a kan hakan.

“Lokacin yin magudi ya wuce yanzu domin an kashe ta’addanci ta hanyar fasaha da tsarinmu, kuma abin da BVAS ya zo cimma kenan.

“Don haka, a zaben 2023, INEC za ta tabbatar da cewa an amince da kuri’un mutanen Osun, ba wai kawai an amince da su ba, har ma da nuna muradin mutanen Osun da Kasar baki ɗaya.

“Babu wanda za a tauye masa hakkinsa na kada kuri’arsa, kuma hukumar za ta yi abin da ya dace a kowane lokaci.” In Ji Shi.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Best seller Channel
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai

https://chat.whatsapp.com/KrigvNKcneVBHxctLUQ0ux

Slide Up
x

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *