Majalisar Dattawa ta fara yunƙurin yin dokar hana amfani da kuɗaɗen waje don farfado da Naira

Canji

Majalisar dattawa ta fara daukar matakai na maido da martabar kudin Najeriya ta hanyar haramta amfani da kudaden ƙasashen waje wajen biyan kudi da hada-hadar kasuwanci a cikin kasar.

Dokar da aka gabatar, da nufin tabbatar da duk biyan kuɗaɗe—da suka hada da albashi da sauran harkoki za a rika gudanar da su da Naira, wani yunkuri na neman farfaɗo da darajar kudaden cikin gida.

Wannan ya hada da sanya wajabcin biyan kudin fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje a Naira.

Sanata Ned Munir Nwoko, shugaban kwamitin majalisar dattijai kan farfaɗo da darajar duniyoyin kasa ne ya dauki nauyin daukar naa.

A cewar Sanata Nwoko, yawaitar amfani da kudaden waje a cikin tsarin hada-hadar kudi na Najeriya na lalata darajar Naira, tare da ci gaba da fuskantar kalubalen tattalin arziki.

Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *