Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya Ta Kori Wani Jamininta Daga Aiki Sakamakon Zane Wani Da Bulala

Alfijr Labarai

Alfijir ta rawaito rundunar ‘yan sandan Najeriya ta kori wani dan sanda mai suna Liyomo Okoi da aka gan shi yana dukan wani mutum da bulala a cikin wani faifan bidiyo da aka yi a watan Yuli a social media

Alfijr Labarai

A cikin faifan bidiyon, Okoi na rike da bindigarsa a hannu daya kuma ya rike bulalar a daya hannun in da ya afkawa mutumin yayin da yake cewa, “Ya yi min barazana.”

Kakakin rundunar, CSP Olumuyiwa Adejobi a wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin ya ce, “Rundunar ta kori jaminin mai lamba 524503 PC Liyomo Okoi da ke aiki a hedikwatar Ekori, rundunar ‘yan sandan jihar Cross Rivers bisa gallazawar da aka dauka a wani faifan bidiyo a ranar 31 ga Yuli, 2022 inda yana yi wa wani mutum bulala.

Alfijr Labarai

korar tasa ta fara aiki daga yau 8 ga watan Agusta, 2022.

Kamar yadda mai magana da yawun yan sanda ya fitar a yau

To gani ga wani ya isa wane tsoron Allah dai.

Slide Up
x