Shugaba Tinubu Ya Naɗa Kwamitin Gudanarwar Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Yamma

Screenshot 20240819 123738 Facebook

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya gabatar da sunayen waɗanda aka zaɓa domin zama a kwamitin farko na hukumar cigaban Yankin Arewa Maso Yamma (NWDC) ga majalisar dattijai domin tantancewa.

Alfijir labarai ta rawaito wannan na biyo bayan sanya hannu kan ƙudirin dokar kafa NWDC da shugaban ya yi a ranar 24 ga Yuli, 2024, a matsayin muhimmin mataki wajen kafuwar hukumar.

Sunayen waɗanda aka naɗa sun haɗa da:

Shugaba: Ambasada Haruna Ginsau (Jigawa)

MD/CEO: Farfesa Abdullahi Shehu Ma’aji (Kano)

Mambobi:

Dr. Yahaya Umar Namahe (Sokoto)

Hon. Aminu Suleiman (Kebbi)

San. Tijani Yahaya Kaura (Zamfara)

Hon. Abdulkadir S. Usman (Kaduna)

Hon. Engr. Muhammad Ali Wudil (Kano)

Shamsu Sule (Katsina)

Nasidi Ali (Jigawa)

Hukumar za ta mayar da hankali wajen samar da cigaban tattalin arziki, bunƙasa rayuwa da cigaban zamantakewa a yankin Arewa Maso Yamma.

Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *