Daraktan cibiyar yaƙi da ta’addanci na ƙasar Amurka ya sanar da ajiye aiki a shafinsa na soshiyal midiya, inda ya ce “tunaninsa bai amince masa ya goyi bayan yaƙin da ake yi kan Iran ba”.
Majalisar dattawan Amurka dai ta tabbatar da Joe Kent a matsayin mutumin da Trump ya zaɓo domin cike gurbin a watan Yulin bara.
Da yake yi wa Trump bayani a wasiƙar ajiye aikin, Kent ya ce “Iran ba ta barazana ga ƙasarmu, kuma a bayyane take cewa mu ne muka fara wannan yaƙi saboda matsin lamba daga Isra’ila da masu neman mata gindin zama masu ƙarfin faɗa a ji.
“Ina goyon bayan akidu da tsare-tsaren ƙasashen waje da ka yi kamfe da su a 2016 da 2020 da 2024 waɗanda kuma ka ɗabbaƙa a zangon mulkinka na farko.
“Har zuwa watan Yunin 2025, ka fahimci cewa yaƙe-yaƙe a Gabas ta Tsakiya tarko ne aka ɗanawa Amurka na ƙarar da rayukan Amerikawa da arziƙi da cigaban dorewar ƙasarmu.
“A matsayina tsohon soja wanda ya je yaƙe-yaƙe har sau 11 kuma mutumin da ya rasa matarsa a yaƙin da Isra’ila da ƙirƙira, babu yadda za a yi na goyi bayan aikewa da matasa domin yin faɗa da ba zai amfani Amurka ba..”
Kawo yanzu dai za a iya cewa Kent ne mutum na farko da ya ajiye aikinsa bisa rashin amincewa da yaƙin da Amurka da Isra’ila suka ƙaddamar kan Iran.
BBC
Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835
Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇
https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t