Za a fuskanci hazo tsawon kwana uku a sassan Najeriya – Hukumar Hasashen Yanayi

FB IMG 1733755101353

Hukumar hasashen yanayi ta Najeriya, NIMET, ta yi hasashen cewa za a fuskanci yanayin hazo da kura a sassan Najeriya daga yau Litinin zuwa Laraba.

Hukumar ta ce yankunan Arewacin dama na tsakiyar Najeriya ne za su fi fuskantar yanayin na hazo da da kura.

NIMET, ta ce za a samu matsala wajen hangen nesa saboda hazon a tsawon kwanakin ukun.

Daga nan hukumar ta bukaci jama’ar da ke zaune yankunan da hazon zai fi tsanani da su dauki matakan kariya musamman wadanda ke fama da wata lalura data shafi rashin kura ko hazo kamar Asma ko kuma cutukan da suka shafi numfashi.

Kazlaika NIMET, ya shawarci kamfanonin jiragen sama da ke zirga-zirga a Najeriya da su tabbata sun samu cikakken rahoton game da yanayin da za a iya kasancewa da shi a iya kwanakin da aka hasashen fuskantar hazo da kurar.

Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *