Badakala! An Tumbuke Kwamishinan Ƴan Sandan Kano , An Maye Gurbinsa Da Sabo

Alfijr ta rawaito Babban Sufeto Janar na ‘yan sandan Najeriya, Alkali Usman, ya mayar da kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano Abubakar Lawal zuwa jihar Ebonyi, biyo bayan zargin cin hanci da wasu manyan jami’an ‘yan sandan jihar suka yi masa.

A wata wasika mai lamba: TH.5361/FS/FHQ/ABJ/V.T3/87 da aka saki da yammacin Juma’a, IGP ya tura kwamishinan ‘yan sandan jihar Ebonyi Aliyu Garba domin ya maye gurbin Mista Usman nan take.

Daily Nigerian ta tattaro cewa manyan jami’an ‘yan sanda a hukumar ‘yan sandan jihar Kano sun koka kan yadda CP ke aikata almundahana, lamarin da ya sa IGP ya bayar da umarnin gudanar da bincike na gaskiya a kan zargin.

Majiyoyin da ke da masaniya kan lamarin sun kuma ce Sufeto Janar din ya kuma tambayi wasu jami’an rundunar da kan sa, wadanda suka tabbatar da zargin da ake yi wa CP.

A cewar majiyoyi na cikin gida, CP, da ya aika zuwa Kano a watan Agusta, ya duba dukkan “harkokin da suka samu riba” a cikin rundunar tare da mika su ofishinsa da kuma “haraji” sassan dabaru da sassan da ke karkashin umurnin “babban mataimakinsa na mako-mako”.

Sabon kwamishinan ‘yan sandan Kano ya kammala karatun digiri na BA History a Jami’ar Sakkwato, kuma ya yi digirin digirgir a fannin shari’a da diflomasiyya a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Port-Harcourt, Jihar Ribas.

Ya shiga aikin ‘yan sandan Nijeriya a shekarar 1990 a matsayin mataimakin Sufeto na ‘yan sanda, Cadet ASP, a makarantar ‘yan sanda (Annex) Jihar Kaduna, inda ya yi horo na tsawon watanni 18 sannan aka tura shi rundunar ‘yan sandan jihar Oyo a matsayin Admin Officer.

Daga nan kuma sai aka mayar da shi Rundunar Jihar Neja a shekarar 1992 inda ya zama ADC ga Gwamnan Jihar Neja a lokacin, Musa Inuwa.

Malam Garba ya yi aiki a bangarori daban-daban na rundunar, ya kuma halarci kwasa-kwasan kwararru da dama a fannin bin doka da oda, hana aikata laifuka da gudanar da ayyuka a ciki da wajen kasar nan.

Ya taba zama mataimakin kwamishinan jin dadin ‘yan sanda, sashen kudi da mulki, hedikwatar rundunar da ke Abuja, hedkwatar rundunar bincike da tsare-tsare ta DCP, Abuja, mataimakin kwamishinan ‘yan sanda na shiyyar 2, Legas.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Best seller Channel
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai

https://chat.whatsapp.com/KrigvNKcneVBHxctLUQ0ux

Slide Up
x

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *