Da Ɗumi-Ɗuminsa: ‘Yan majalisar wakilan Nijeriya 17 sun fice daga jam’iyyar ADC zuwa NDC

IMG 132940 05526 1777984188024

Editor

Akalla ‘yan majalisar wakilan Nijeriya 17 sun sauya sheka daga jam’iyyar ADC zuwa jam’iyyar NDC.

An sanar da sauya shekar tasu ne a zauren majalisar yayin zamanta a ranar Talata, inda a hannu guda aka sanar da sauya shekar Leke Abejide daga ADC zuwa jam’iyyar APC.

‘Yan majalisar da suka koma NDC sun hada da Yusuf Datti, Uchenna Okonkwo, Adamu Wakili, Thaddeus Attah, George Ozodinobi, Lilian Orogbu, Oluwaseyi Sowunmi, Peter Aniekwe, Mukhtar Zakari, George Oluwande da Munachim Umezuruike.

Sauran sun hada da Emeka Idu, Jesse Onuakalusi, Ifeanyi Uzokwe, Afam Ogene da Abdulhakeem Ado, kamar yadda gidan talabijin na Channels ya ruwaito.

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *