Dattawan Yankin Neja Delta Sun Gargadi Ministan Shari’a Malami San

Alfijr ta rawaito dattawan yankin Neja (SSEPF) a jiya sun bukaci babban mai shari’a na tarayya kuma ministan shari’a, Abubakar Malami (SAN) da ya ci gaba da bin ka’idojin da suka dace a wajen nadin mukaddashin Manajan Darakta na Hukumar Raya Yankin Neja Delta (NDDC).

Alfijr Labarai

Kungiyar ta SSEPF wacce mambobinta ta kunshi dattawan jihohin Neja Delta, ta yi gargadin cewa rashin yin hakan zai jefa yankin cikin wani rikici, wanda za a dorawa ministan alhakinsa.

Kungiyar, a cikin wata sanarwa, ta ce idan aka bi karba-karba, jihar Bayelsa ce ta samar da NDDC MD.

Sanarwar ta samu sa hannun hadin guiwar shugaban kungiyar, Dokta Promise Okpolo da kuma ko odinetan hulda da jama’a, Cif Anderson Etiwo.

In da ya nuna fargabar cewa shawarar da ministar ta baiwa shugaban kasa Muhammadu Buhari akan kundin tsarin mulki na hukumar NDDC ta sabawa tsarin karba-karba, inda ta kara da cewa irin wannan shawarar za ta yaudari shugaban kasa.

Alfijr Labarai

Ta ce damuwarta ta samo asali ne daga abin da ta yi imani da cewa ofishin AGF na “kurman baki” na sashe na 12 (1) na dokar NDDC ta 2000 da ya shafi nadin shugaban hukumar.

Sashe na 12 (1) na dokar ya nuna cewa: “Akwai hukumar, Manajan Darakta, da manyan daraktoci guda biyu wadanda za su kasance ‘yan asalin yankunan da ake hako mai da suka fara daga kasashe mambobin hukumar da ke da yawan man fetur, kuma za su juya tsakanin ƙasashe membobin cikin tsari na samarwa

Slide Up
x