Da Ɗumi Ɗuminsa! Gwamna El-Rufai Ya Bada Umarnin Rushe Garuruwa Uku Da Ke Baiwa ‘Yan Bindiga mafaka a titin Kaduna zuwa Abuja.

Alfijr

Alfijr ta rawaito gwamnatin Jihar Kaduna ta ce za ta yi la’akari da yanayin ko dai ta sake tsugunar da mazauna unguwanni ko kuma ta rushe unguwanni uku da ke kan hanyar Abuja zuwa Kaduna sakamakon hare-haren da ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda ke kaiwa matafiya. a wannan yanki.

Garuruwa ukun sun hada da Rijana, Kateri da Akilibu, dukkansu a karamar hukumar Kagarko.

Gwamna Nasir El-Rufai, a wata tattaunawa da yayi da Channel Tv ya koka da yadda ake samun karin ‘yan bindiga a yankunan, ya ce amsa kawai ita ce jami’an tsaro su duba zabin da suka hada da yadda za a rushe garuruwa uku gaba daya da kuma mayar da mazauna garuruwa wasu matsugunan.

Alfijr

Ya kara da cewar damuwa ta farko da nake gani daga wannan rahoto shine ci gaba da ambaton Rijana, Kateri da Akilibu a duk wadannan laifuka, musamman tsaro ko rashin sa akan hanyar Abuja zuwa Kaduna.

Mun yi ta binciken abin da za mu yi kan wadannan matsugunan guda uku, ko za a mayar da su kusa da Kagarko, ko za a share matsugunan gaba daya, kuma ina son kwamitin sulhu ya yi shawara kan wannan kuma mu duba zabin, inji El Rufa i

Alfijr

Gwamnan ya bayyana cewa, bayanan sirrin da ya samu sun nuna cewa wasu mazauna cikin al’ummomin suna aikin ‘yan bindiga ne da ‘yan ta’adda, don haka hare-haren da ake kai wa kan hanyar Kaduna zuwa Abuja ya Kara tsananta

El-Rufai ya kara da cewa, “A bayyane yake cewa akwai manyan jami’an leken asiri da masu aikata laifuka a wadannan wurare.

Alfijr

Me ya sa a duk lokacin da aka kai hari ko sace mutane a hanyar Abuja zuwa Kaduna, hakan kan faru ne a kan hanyar nan ta uku kuma babu wani abu da ya taba faruwa a bangaren Kagarko “Akwai matsala a wadannan matsugunai guda uku kuma bai kamata gwamnati ta ki yin komai ba, ko ta kasa yin komai.

Dole ne mu duba zabin da ya hada da share matsugunan gaba daya da kuma mayar da jama’a zuwa inda sauran masu gaskiya suke zaune.

Alfijr

Gwamnan ya kuma nuna damuwarsa kan yadda ta’ammali da miyagun kwayoyi ke afkuwa wajen tabarbarewar tsaro a jihar Kaduna.

Don haka ya umurci jami’an tsaro da su farauto irin wadannan mutane da nufin gurfanar da su a gaban kuliya da kuma yanke musu hanyoyin samar da kayayyakin maye.

Slide Up
x