Gwamnan Kano ya kaddamar da aikin gyaran manyan tituna 17 a faɗin jihar

FB IMG 1741452920961

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da aikin gyaran titin da ya tashi daga club road zuwa titin airport a karkashin shirinsa na gyara manyan titunan kwaryar  birnin Kano.

Da yake jawabi a wajen kaddamar da aikin, gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce gwamnati zata gyara manyan tituna 17 domin inganta sufuri da habaka tattalin arzikin jihar Kano.

Gwamnan ya kara da cewa, gyaran titunan zasu rage afkuwar hadurra a tituna wanda ke haddasa hasarar rayuka da dukiyoyin al’uma.

Ya bukaci kamfanin da zai gudanar da aikin dasu aiwatar da aiki mai nagarta, yana mai jaddada cewa gwamnatinsa ba zata lamunci almindahna ko kuma aiki mara inganci ba.

A jawabinsa shugaban karamar hukumar Nassarawa Alhaji Yusuf Imam Ogan Boye  wanda kuma shi ne mataimakin shugabar  kungiyar shugabannin kananan hukumomin cikin kyaryar birnin Kano ya godewa gwamna Abba Kabir Yusuf bisa yunkurinsa na kyautata titunan birnin Kano.

RK

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news zaku iya bibiyarmu ta 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/IqPyC2oGzdQ9NudcMXFqHZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *