Ganduje Ya Baiwa Masu Neman Tsayawa Takara Wa’adin Sa’o’i 24 Su Ajiye Ayyukansu, Tuni Wasu Sun ajiye

Alfijr

Alfijr ta rawaito Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya bayar da wa’adin sa’o’i 24 ga duk wani dan siyasa da ke neman tsayawa takara a Zabe mai zuwa na 2023.

Sanarwar da Abbas Anwar ya fitar, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya Umarci duk Wani Dake Rike da Mukamin Siyasa a Gwamnatin sa kuma yake son Takara daya aje aikinsa daga yanzu zuwa Litinin 18 ga watan Afrilu da muke ciki.

Cikin wata Sanarwa mai dauke dasa hannun Daraktan Yada Labaran Gwamna, Malam Abba Anwar yace Hakan ha zama wajibi duba da tanade tanaden Sashi na 84 (12) cikin Baka na Sabuwar Dokar Zaɓen Kasar nan.

Alfijr

Kadan daga cikin wadanda suka fara sauka a yau.

Hon Musa Iliyasu

Hon Murtala Sule Garo

Hon Nuraq Muhammadu Dan kadai

Hon Faruk Sule Garo

Hon Mukhtar Ishaq Yakasai

Hon Sanusi Sa’idu Kiru

Hon Ibrahim Ahmad Karaye

Slide Up
x