![](https://alfijr.com.ng/wp-content/uploads/2022/04/FB_IMG_1650545347255.jpg)
Alfijr ta rawaito rundunar sojin Najeriya ta sake kama wani kasurgumin dan ta’addan da aka dade ana nema ruwa a jallo
![](https://alfijr.com.ng/wp-content/uploads/2022/04/IMG_20220212_150753-20-650x141.jpg)
An kama Modu Babagana ne a karo na biyu bayan ya tsere daga gidan gyaran halib da aka ajiye shi a shekarar 2020
A yanzu da aka sake kama shi, an kama shi ne lokacin da yake siyayya ga ‘yan ta’addan Boko Haram
![](https://alfijr.com.ng/wp-content/uploads/2022/04/FB_IMG_1650545338639.jpg)
Alfijr
Dakarun runduna ta musamman ta 21 dake garin Bama aa jihar Borno sun kama kasurgumin dan leken asiri da ake nema ruwa a jallo na ‘yan ta’addar Boko Haram/ISWAP, Modu Babagana, wanda ya tsere daga hannun sojoji a garin Bama ta jihar Barno.
An kama fitaccen dan ta’addan ne a baya a watan Janairun 2020 da laifin aikita leken asiri kan sojoji a yankin Bama da Banki.
Kamar yadda Leadership ta wallafa
Slide Up