Da Dumi Duminsa! Kotua Ta Soke Belin Dan Sarauniya Ta Ba Da Umarnin A Kama Shi

Alfijr

Yanzu-yanzu: Kotu ta soke belin Ganduje, ta kuma ba da umarnin a kama shi

Kotun Majistare ta Jihar Kano mai lamba 58 karkashin jagorancin Aminu Gabari ta soke belin da ta bayar tun da farko ga mai sukar Ganduje a shafukan sada zumunta, Mu’a’zu Magaji Dansarauniya kan rashin halartar kotun har sau 3 domin amsa tuhumar da ake masa.

Hakazalika kotun ta bayar da umarnin a kama shi da laifin bata sunan gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, tare da kira ga masu tsaya masa guda biyu da su bayyana ranar 28 ga watan Maris.

Slide Up
x